< Zabura 14 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Wawaye sukan ce a ransu, “Ba Allah.” Sun lalace, ayyukansu kuwa mugaye ne; babu wani da yake yi abu mai kyau.
To the Overseer. — By David. A fool hath said in his heart, 'God is not;' They have done corruptly, They have done abominable actions, There is not a doer of good.
2 Ubangiji ya duba daga sama a kan’yan adam don yă ga ko akwai wani da ya gane, wani wanda yake neman Allah.
Jehovah from the heavens Hath looked on the sons of men, To see if there is a wise one — seeking God.
3 Duka sun kauce, duka gaba ɗaya sun zama lalatattu; babu ɗaya wanda yake yin abu mai kyau, ba ko ɗaya.
The whole have turned aside, Together they have been filthy: There is not a doer of good, not even one.
4 Masu aikata mugunta za su taɓa koyo. Suna cin mutane yadda mutane ke cin gurasa kuma waɗanda ba sa kira bisa Ubangiji?
Have all working iniquity not known? Those consuming my people have eaten bread, Jehovah they have not called.
5 Ga su, tsoro ya sha kansu, gama Allah yana cikin ƙungiyar adalai.
There they have feared a fear, For God [is] in the generation of the righteous.
6 Ku masu mugunta kuna sa ƙoƙarin matalauta yă zama banza, amma Ubangiji ne mafakansu.
The counsel of the poor ye cause to stink, Because Jehovah [is] his refuge.
7 Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Ubangiji zai maido da sa’ar mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!
'Who doth give from Zion the salvation of Israel? When Jehovah doth turn back [To] a captivity of His people, Jacob doth rejoice — Israel is glad!

< Zabura 14 >