< Zabura 14 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Wawaye sukan ce a ransu, “Ba Allah.” Sun lalace, ayyukansu kuwa mugaye ne; babu wani da yake yi abu mai kyau.
To the Chief Musician. David’s. The impious hath said in his heart—There is no God! They have acted corruptly, they have done an abominable deed, there is none that doeth good.
2 Ubangiji ya duba daga sama a kan’yan adam don yă ga ko akwai wani da ya gane, wani wanda yake neman Allah.
Yahweh, out of the heavens, looked down over the sons of men, —to see whether there was one that showed wisdom, enquiring after God: —
3 Duka sun kauce, duka gaba ɗaya sun zama lalatattu; babu ɗaya wanda yake yin abu mai kyau, ba ko ɗaya.
The whole, have turned aside, Together have they become tainted, —There is none that doeth good, not so much as, one!
4 Masu aikata mugunta za su taɓa koyo. Suna cin mutane yadda mutane ke cin gurasa kuma waɗanda ba sa kira bisa Ubangiji?
Are all the workers of iniquity, without knowledge? devouring my people [as] they devour food! Upon Yahweh, have they not called.
5 Ga su, tsoro ya sha kansu, gama Allah yana cikin ƙungiyar adalai.
There have they been in great dread, because, God, is in the circle of the righteous man.
6 Ku masu mugunta kuna sa ƙoƙarin matalauta yă zama banza, amma Ubangiji ne mafakansu.
The purpose of the poor, ye would put to shame, because, Yahweh, is his refuge.
7 Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Ubangiji zai maido da sa’ar mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!
Oh that, out of Zion, were granted the salvation of Israel! When Yahweh bringeth back the captives of his people, Jacob, shall exult, Israel, be glad.