< Zabura 14 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Wawaye sukan ce a ransu, “Ba Allah.” Sun lalace, ayyukansu kuwa mugaye ne; babu wani da yake yi abu mai kyau.
For the leader. Of David. Fools say in their heart, “There is no God.” Vile, hateful their life is; not one does good.
2 Ubangiji ya duba daga sama a kan’yan adam don yă ga ko akwai wani da ya gane, wani wanda yake neman Allah.
From heaven the Lord looks out on humans, to see if any are wise, and care for God.
3 Duka sun kauce, duka gaba ɗaya sun zama lalatattu; babu ɗaya wanda yake yin abu mai kyau, ba ko ɗaya.
But all have turned bad, the taint is on all; not one does good, no, not one.
4 Masu aikata mugunta za su taɓa koyo. Suna cin mutane yadda mutane ke cin gurasa kuma waɗanda ba sa kira bisa Ubangiji?
Have they learned their lesson, those workers of evil? Who ate up my people, eating, devouring, never calling to the Lord.
5 Ga su, tsoro ya sha kansu, gama Allah yana cikin ƙungiyar adalai.
Sore afraid will they be; for God is among those who are righteous,
6 Ku masu mugunta kuna sa ƙoƙarin matalauta yă zama banza, amma Ubangiji ne mafakansu.
you may mock the plans of the poor, but the Lord is their refuge.
7 Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Ubangiji zai maido da sa’ar mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!
If only help from Zion would come for Israel! When the Lord brings his people a change of fortune, how glad will be Jacob, and Israel how joyful!