< Zabura 14 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Wawaye sukan ce a ransu, “Ba Allah.” Sun lalace, ayyukansu kuwa mugaye ne; babu wani da yake yi abu mai kyau.
For the Leader. A Psalm of David. The fool hath said in his heart: 'There is no God'; they have dealt corruptly, they have done abominably; there is none that doeth good.
2 Ubangiji ya duba daga sama a kan’yan adam don yă ga ko akwai wani da ya gane, wani wanda yake neman Allah.
The LORD looked forth from heaven upon the children of men, to see if there were any man of understanding, that did seek after God.
3 Duka sun kauce, duka gaba ɗaya sun zama lalatattu; babu ɗaya wanda yake yin abu mai kyau, ba ko ɗaya.
They are all corrupt, they are together become impure; there is none that doeth good, no, not one.
4 Masu aikata mugunta za su taɓa koyo. Suna cin mutane yadda mutane ke cin gurasa kuma waɗanda ba sa kira bisa Ubangiji?
'Shall not all the workers of iniquity know it, who eat up My people as they eat bread, and call not upon the LORD?'
5 Ga su, tsoro ya sha kansu, gama Allah yana cikin ƙungiyar adalai.
There are they in great fear; for God is with the righteous generation.
6 Ku masu mugunta kuna sa ƙoƙarin matalauta yă zama banza, amma Ubangiji ne mafakansu.
Ye would put to shame the counsel of the poor, but the LORD is his refuge.
7 Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Ubangiji zai maido da sa’ar mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!
Oh that the salvation of Israel were come out of Zion! When the LORD turneth the captivity of His people, let Jacob rejoice, let Israel be glad.