< Zabura 14 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Wawaye sukan ce a ransu, “Ba Allah.” Sun lalace, ayyukansu kuwa mugaye ne; babu wani da yake yi abu mai kyau.
To the chief music-maker. Of David. The foolish man has said in his heart, God will not do anything. They are unclean, they have done evil works; there is not one who does good.
2 Ubangiji ya duba daga sama a kan’yan adam don yă ga ko akwai wani da ya gane, wani wanda yake neman Allah.
The Lord was looking down from heaven on the children of men, to see if there were any who had wisdom, searching after God.
3 Duka sun kauce, duka gaba ɗaya sun zama lalatattu; babu ɗaya wanda yake yin abu mai kyau, ba ko ɗaya.
They have all gone out of the way together; they are unclean, there is not one who does good, no, not one.
4 Masu aikata mugunta za su taɓa koyo. Suna cin mutane yadda mutane ke cin gurasa kuma waɗanda ba sa kira bisa Ubangiji?
Have all the workers of evil no knowledge? they take my people for food as they would take bread; they make no prayer to the Lord.
5 Ga su, tsoro ya sha kansu, gama Allah yana cikin ƙungiyar adalai.
Then were they in great fear: for God is in the generation of the upright.
6 Ku masu mugunta kuna sa ƙoƙarin matalauta yă zama banza, amma Ubangiji ne mafakansu.
You have put to shame the thoughts of the poor, but the Lord is his support.
7 Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Ubangiji zai maido da sa’ar mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!
May the salvation of Israel come out of Zion! when the fate of his people is changed by the Lord, Jacob will have joy and Israel will be glad.