< Zabura 139 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
Salmo de Davi, para o regente: SENHOR, tu me examinas e me conheces.
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
Tu sabes o meu sentar e o meu caminhar; de longe entendes meus pensamentos.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
Tu cercas o meu andar e meu deitar; conheces desde antes os meus caminhos.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
Mesmo não havendo [ainda] palavra [alguma] em minha língua, eis, SENHOR, que já sabes tudo.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
Tu me envolves por detrás e pela frente, e pões tua mão sobre mim.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
[Teu] conhecimento é maravilhoso demais para mim, tão alto que não posso [alcançá] -lo.
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Para onde eu escaparia de teu Espírito? E para onde fugiria de tua presença?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol )
Se eu subisse até os céus, lá tu [estás]; se eu fizer meu leito no Xeol, eis que tu [também ali estás]. (Sheol )
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
Se eu tomasse as asas do amanhecer, e morasse nas extremidades do mar,
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
Até ali tua mão me guiaria, e tua mão direita me seguraria.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
Se eu dissesse: Certamente as trevas me encobrirão; e a luz ao redor de mim [será como] a noite.
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
Porém nem mesmo as trevas [me] esconderão de ti; ao invés disso, [pois] a noite é tão clara quanto o dia, [e aos teus olhos] as trevas são como a luz.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
Porque tu és dono do meu ser, e me cobriste no ventre da minha mãe.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
Eu te louvarei porque de um [jeito] assombroso e maravilhoso eu fui feito; maravilhosas [são] tuas obras; e minha alma sabe muito bem.
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
Meus ossos não estavam escondidos de ti quando eu fui feito em oculto, e formado como tramas de tecido nas profundezas da terra.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Teus olhos viram meu corpo [ainda] sem forma, e tudo estava escrito em teu livro; [até] os dias estavam determinados quando nenhum deles [ainda] havia.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
Como são preciosos para mim os teus pensamentos, Deus! Como é grande a quantidade deles!
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
Se eu os contasse, seriam muito mais [numerosos] que a areia; [quando] acordo, ainda estou contigo.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
Ah, Deus, tomara que mates ao perverso! E vós, homens sanguinários, afastai-vos de mim;
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
Porque eles falam de ti com maldade, [e] teus inimigos [se] exaltam em vão.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Por acaso, SENHOR, eu não odiaria aos que te odeiam? E não detestaria os que se levantam contra ti?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
Eu os odeio com ódio completo; eu os considero como inimigos.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Examina-me, Deus, e conhece meu coração; prova-me, e conhece meus pensamentos.
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
E vê se em mim [há algum] mau caminho; e guia-me pelo caminho eterno.