< Zabura 139 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
in finem David psalmus
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
Domine probasti me et cognovisti me tu cognovisti sessionem meam et surrectionem meam
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
intellexisti cogitationes meas de longe semitam meam et funiculum meum investigasti
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
et omnes vias meas praevidisti quia non est sermo in lingua mea
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
ecce Domine tu cognovisti omnia novissima et antiqua tu formasti me et posuisti super me manum tuam
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
mirabilis facta est scientia tua ex me confortata est non potero ad eam
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
quo ibo ab spiritu tuo et quo a facie tua fugiam
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol )
si ascendero in caelum tu illic es si descendero ad infernum ades (Sheol )
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
si sumpsero pinnas meas diluculo et habitavero in extremis maris
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
etenim illuc manus tua deducet me et tenebit me dextera tua
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
et dixi forsitan tenebrae conculcabunt me et nox inluminatio in deliciis meis
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
quia tenebrae non obscurabuntur a te et nox sicut dies inluminabitur sicut tenebrae eius ita et lumen eius
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
quia tu possedisti renes meos suscepisti me de utero matris meae
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
confitebor tibi quia terribiliter magnificatus es mirabilia opera tua et anima mea cognoscit nimis
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
non est occultatum os meum a te quod fecisti in occulto et substantia mea in inferioribus terrae
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
inperfectum meum viderunt oculi tui et in libro tuo omnes scribentur die formabuntur et nemo in eis
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
mihi autem nimis honorificati sunt amici tui Deus nimis confirmati sunt principatus eorum
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
dinumerabo eos et super harenam multiplicabuntur exsurrexi et adhuc sum tecum
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
si occideris Deus peccatores et viri sanguinum declinate a me
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
quia dices in cogitatione accipient in vanitate civitates tuas
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
nonne qui oderunt te Domine oderam et super inimicos tuos tabescebam
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
perfecto odio oderam illos inimici facti sunt mihi
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
proba me Deus et scito cor meum interroga me et cognosce semitas meas
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
et vide si via iniquitatis in me est et deduc me in via aeterna