< Zabura 139 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
Untuk pemimpin kor. Mazmur Daud. Ya TUHAN, Engkau menyelami aku dan mengenal aku.
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
Engkau tahu segala perbuatanku; dari jauh Engkau mengerti pikiranku.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
Engkau melihat aku, baik aku bekerja atau beristirahat, Engkau tahu segala yang kuperbuat.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
Bahkan sebelum aku berbicara, Engkau tahu apa yang hendak kukatakan.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
Engkau mengelilingi aku dari segala penjuru, dan Kaulindungi aku dengan kuasa-Mu.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Terlalu dalam bagiku pengetahuan-Mu itu, tidak terjangkau oleh pikiranku.
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Ke mana aku dapat pergi agar luput dari kuasa-Mu? Ke mana aku dapat lari menjauh dari hadapan-Mu?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
Jika aku naik ke langit, Engkau ada di sana, jika aku tidur di alam maut, di situ pun Engkau ada. (Sheol h7585)
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
Jika aku terbang lewat ufuk timur atau berdiam di ujung barat yang paling jauh,
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
di sana pun Engkau menolong aku; di sana juga tangan-Mu membimbing aku.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
Jika aku minta supaya gelap menyelubungi aku, dan terang di sekelilingku menjadi malam,
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
maka kegelapan itu pun tidak gelap bagi-Mu; malam itu terang seperti siang, dan gelap itu seperti terang.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
Engkau menciptakan setiap bagian badanku, dan membentuk aku dalam rahim ibuku.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
Aku memuji Engkau sebab aku sangat luar biasa! Segala perbuatan-Mu ajaib dan mengagumkan, aku benar-benar menyadarinya.
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
Waktu tulang-tulangku dijadikan, dengan cermat dirangkaikan dalam rahim ibuku, sedang aku tumbuh di sana secara rahasia, aku tidak tersembunyi bagi-Mu.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Engkau melihat aku waktu aku masih dalam kandungan; semuanya tercatat di dalam buku-Mu; hari-harinya sudah ditentukan sebelum satu pun mulai.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
Betapa sulitnya pikiran-Mu bagiku, ya Allah, dan betapa banyak jumlahnya!
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
Jika kuhitung, lebih banyak dari pasir; bila aku bangun, masih juga kupikirkan Engkau.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
Kiranya orang jahat Kautumpas, ya Allah, jauhkanlah para penumpah darah daripadaku!
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
Mereka mengatakan yang jahat tentang Engkau, dan bersumpah palsu demi kota-kota-Mu.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Ya TUHAN, kubenci orang yang membenci Engkau, hatiku kesal terhadap orang yang melawan Engkau!
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
Mereka sangat kubenci, dan kuanggap sebagai musuh.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Selidikilah aku ya Allah, selamilah hatiku, ujilah aku dan ketahuilah pikiranku.
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
Lihatlah entah ada kejahatan dalam diriku, dan bimbinglah aku di jalan yang kekal.

< Zabura 139 >