< Zabura 139 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
Dem Vorsänger. Ein Psalm Davids. HERR, du hast mich erforscht und kennst mich!
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
Ich sitze oder stehe, so weißt du es; du merkst meine Gedanken von ferne.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
Du beobachtest mich, ob ich gehe oder liege, und bist vertraut mit allen meinen Wegen;
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
ja es ist kein Wort auf meiner Zunge, das du, HERR, nicht völlig wüßtest!
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
Von hinten und von vorn hast du mich eingeschlossen und deine Hand auf mich gelegt.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Diese Erkenntnis ist mir zu wunderbar, zu hoch, als daß ich sie fassen könnte!
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Wo soll ich hingehen vor deinem Geist, wo soll ich hinfliehen vor deinem Angesicht?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol )
Führe ich zum Himmel, so bist du da; bettete ich mir im Totenreich, siehe, so bist du auch da! (Sheol )
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
Nähme ich Flügel der Morgenröte und bliebe am äußersten Meer,
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
so würde auch daselbst deine Hand mich führen und deine Rechte mich halten!
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
Spräche ich: «Finsternis möge mich überfallen und das Licht zur Nacht werden um mich her!»,
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
so ist auch die Finsternis nicht finster für dich, und die Nacht leuchtet wie der Tag; Finsternis ist wie das Licht.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
Denn du hast meine Nieren geschaffen, du wobest mich in meiner Mutter Schoß.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
Ich danke dir, daß du mich wunderbar gemacht hast; wunderbar sind deine Werke, und meine Seele erkennt das wohl!
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
Mein Gebein war dir nicht verhohlen, da ich im Verborgenen gemacht ward, gewirkt tief unten auf Erden.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Deine Augen sahen mich, als ich noch unentwickelt war, und es waren alle Tage in dein Buch geschrieben, die noch werden sollten, als derselben noch keiner war.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
Und wie teuer sind mir, o Gott, deine Gedanken! Wie groß ist ihre Summe!
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
Wollte ich sie zählen, so würde ihrer mehr sein als der Sand. Wenn ich erwache, so bin ich noch bei dir!
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
Ach Gott, daß du den Gottlosen tötetest und die Blutgierigen von mir weichen müßten!
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
Denn sie empören sich arglistig wider dich; deine Feinde erheben [ihre Hand] zur Lüge.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Sollte ich nicht hassen, die dich, HERR, hassen, und keinen Abscheu empfinden vor deinen Widersachern?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
Ich hasse sie mit vollkommenem Haß, sie sind mir zu Feinden geworden.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Erforsche mich, o Gott, und erkenne mein Herz; prüfe mich und erkenne, wie ich es meine;
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
und siehe, ob ich auf bösem Wege bin, und leite mich auf ewigem Wege!