< Zabura 139 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
Pour la fin, psaume de David.
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
C’est vous qui avez connu mon coucher et mon lever.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
Vous avez compris de loin mes pensées; vous avez observé mes sentiers et le cours de ma vie.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
Et toutes mes voies, vous les avez prévues; car il n’y a point de parole sur ma langue.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
Voilà que vous. Seigneur, vous avez connu toutes les choses nouvelles et anciennes: c’est vous qui m’avez formé, et qui avez mis sur moi votre main.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Votre science est devenue admirable pour moi: elle est affermie, et je ne pourrai pas y atteindre.
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Où irai-je pour me dérober à votre esprit? où fuirai-je devant votre face?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol )
Si je monte au ciel, vous y êtes; si je descends dans l’enfer, vous y êtes présent. (Sheol )
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
Si je prends mes ailes au point du jour, et que j’habite aux extrémités de la mer,
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
Là encore votre main me conduira, et votre droite me retiendra.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
Et j’ai dit: Peut-être que les ténèbres me couvriront; et la nuit est une lumière autour de moi dans mes plaisirs,
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
Parce que les ténèbres ne seront pas obscures pour vous, et la nuit sera éclairée comme le jour: comme sont les ténèbres de celle-là, de même aussi est la lumière de celui-ci.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
Parce que c’est vous qui êtes en possession de mes reins, vous m’avez reçu dès le sein de ma mère.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
Je vous glorifierai, parce que vous avez montré d’une manière terrible votre magnificence: admirables sont vos œuvres, mon âme le reconnaît parfaitement.
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
Mes os n’ont pas été cachés pour vous qui les avez faits dans le secret; ni ma substance formée dans les parties inférieures de la terre.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Vos yeux ont vu mon corps encore informe, et tous les hommes seront écrits dans votre livre: il se formera des jours, dans lesquels il n’y aura personne.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
Mais pour moi, ô Dieu, vos amis sont devenus extrêmement honorables; leur empire s’est extrêmement fortifié.
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
Je les compterai, et ils se trouveront plus nombreux que le sable: je me suis réveillé, et je suis encore avec vous.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
Si vous tuez les pécheurs, ô Dieu, hommes de sang, détournez-vous de moi;
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
Parce que vous dites dans votre pensée: Ils recevront en vain vos cités.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Est-ce que je n’ai pas haï, Seigneur, ceux qui vous haïssaient; et au sujet de vos ennemis, ne séchais-je pas?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
Je les haïssais d’une haine parfaite; et ils sont devenus des ennemis pour moi.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Eprouvez-moi, ô Dieu, et comprenez mon cœur: interrogez-moi et connaissez mes sentiers.
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
Et voyez si une voie d’iniquité est en moi, et conduisez-moi dans la voie éternelle.