< Zabura 139 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
To the Chief Musician, David’s. A Melody. O Yahweh! thou hast searched me, and observed:
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
Thou, hast observed my downsitting and mine uprising, Thou hast given heed to my desire, from afar:
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
My path and my couch, hast thou examined, and, all my ways, thou well knowest.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
Surely there hath not been a word on my tongue, [but] behold! O Yahweh, thou hast observed it on every side.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
Behind and before, hast thou shut me in, and hast laid upon me thy hand: —
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Knowledge, too wonderful, for me! high, I cannot attain to it!
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Whither can I go from thy spirit? or whither, from thy face, can I flee?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
If I ascend the heavens, there, thou art! If I spread out hades as my couch, behold thee! (Sheol h7585)
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
If I mount the wings of the dawn, settle down in the region beyond the sea,
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
Even there, thy hand shall lead me, and thy right hand shall hold me.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
If I say, Surely, darkness, shall cover me! then, night, is light about me.
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
Even darkness, will not conceal from thee, —but, night, like day, will shine, So is the darkness, as the light!
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
For, thou, didst possess thyself of my reins, thou didst weave me together in the womb of my mother.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
I thank thee, in that fearfully was my being distinguished, Wonderful are thy works, and, mine own soul, is observing [them] intently!
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
My substance was not hid from thee, —when I was made in secret, when I was skilfully figured in the lower parts of the earth.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Mine unfinished substance, thine eyes beheld, and, in thy book, all the parts thereof were written, —the days they should be fashioned! while yet there was not one among them.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
To me, then, how precious have thy desires become, O GOD! How numerous, the heads of them!
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
I would recount them! Beyond the sands, they multiply, I rouse myself—and am still with thee.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
Wilt thou not, O GOD, slay the lawless one? Therefore, ye men of bloodshed, depart from me!
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
For they speak of thee wickedly, Thy foes lift up [their hand] unto falsehood.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Do I not hate, them who hate thee, O Yahweh? And loathe, them who rise up against thee?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
With completeness of hatred, I hate them, As enemies, have they become to me.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Search me, O GOD, and observe my heart, Try me, and observe my cares;
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
And see if there be any idol-way in me, and lead me in a way age-abiding.

< Zabura 139 >