< Zabura 139 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
“For the leader of the music. A psalm of David.” O LORD! thou hast searched me and known me!
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
Thou knowest my sitting-down and my rising-up; Thou understandest my thoughts from afar!
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
Thou seest my path and my lying-down, And art acquainted with all my ways!
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
For before the word is upon my tongue, Behold, O LORD! thou knowest it altogether!
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
Thou besettest me behind and before, And layest thine hand upon me!
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Such knowledge is too wonderful for me; It is high, I cannot attain to it!
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Whither shall I go from thy spirit, And whither shall I flee from thy presence?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
If I ascend into heaven, thou art there! If I make my bed in the underworld, behold, thou art there! (Sheol h7585)
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
If I take the wings of the morning, And dwell in the remotest parts of the sea,
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
Even there shall thy hand lead me, And thy right hand shall hold me!
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
If I say, “Surely the darkness shall cover me;” Even the night shall be light about me.
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
Yea, the darkness hideth not from thee, But the night shineth as the day; The darkness and the light are both alike to thee!
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
For thou didst form my reins; Thou didst weave me in my mother's womb.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
I will praise thee; for I am fearfully and wonderfully made; Marvellous are thy works, And this my soul knoweth full well!
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
My frame was not hidden from thee, When I was made in secret. When I was curiously wrought in the lower parts of the earth.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Thine eyes did see my substance, while yet unformed, And in thy book was every thing written; My days were appointed before one of them existed.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
How precious to me are thy thoughts, O God! How great is the sum of them!
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
If I should count them, they would outnumber the sand: When I awake, I am still with thee!
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
O that thou wouldst slay the wicked, O God! Ye men of blood, depart from me!
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
For they speak against thee wickedly; Thine enemies utter thy name for falsehood.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Do I not hate them that hate thee, O LORD? Do I not abhor them that rise up against thee?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
Yea, I hate them with perfect hatred; I count them mine enemies.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Search me, O God! and know my heart; Try me, and know my thoughts;
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
And see if the way of trouble be within me, And lead me in the way everlasting!

< Zabura 139 >