< Zabura 139 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
To the chief music-maker. A Psalm. Of David. O Lord, you have knowledge of me, searching out all my secrets.
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
You have knowledge when I am seated and when I get up, you see my thoughts from far away.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
You keep watch over my steps and my sleep, and have knowledge of all my ways.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
For there is not a word on my tongue which is not clear to you, O Lord.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
I am shut in by you on every side, and you have put your hand on me.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Such knowledge is a wonder greater than my powers; it is so high that I may not come near it.
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Where may I go from your spirit? how may I go in flight from you?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
If I go up to heaven, you are there: or if I make my bed in the underworld, you are there. (Sheol h7585)
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
If I take the wings of the morning, and go to the farthest parts of the sea;
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
Even there will I be guided by your hand, and your right hand will keep me.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
If I say, Only let me be covered by the dark, and the light about me be night;
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
Even the dark is not dark to you; the night is as bright as the day: for dark and light are the same to you.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
My flesh was made by you, and my parts joined together in my mother's body.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
I will give you praise, for I am strangely and delicately formed; your works are great wonders, and of this my soul is fully conscious.
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
My frame was not unseen by you when I was made secretly, and strangely formed in the lowest parts of the earth.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Your eyes saw my unformed substance; in your book all my days were recorded, even those which were purposed before they had come into being.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
How dear are your thoughts to me, O God! how great is the number of them!
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
If I made up their number, it would be more than the grains of sand; when I am awake, I am still with you.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
If only you would put the sinners to death, O God; go far from me, you men of blood.
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
For they go against you with evil designs, and your haters make sport of your name.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Are not your haters hated by me, O Lord? are not those who are lifted up against you a cause of grief to me?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
My hate for them is complete; my thoughts of them are as if they were making war on me.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
O God, let the secrets of my heart be uncovered, and let my wandering thoughts be tested:
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
See if there is any way of sorrow in me, and be my guide in the eternal way.

< Zabura 139 >