< Zabura 139 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
For the choirmaster. A Psalm of David. O LORD, You have searched me and known me.
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
You know when I sit and when I rise; You understand my thoughts from afar.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
You search out my path and my lying down; You are aware of all my ways.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
Even before a word is on my tongue, You know all about it, O LORD.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
You hem me in behind and before; You have laid Your hand upon me.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Such knowledge is too wonderful for me, too lofty for me to attain.
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Where can I go to escape Your Spirit? Where can I flee from Your presence?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
If I ascend to the heavens, You are there; if I make my bed in Sheol, You are there. (Sheol h7585)
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
If I rise on the wings of the dawn, if I settle by the farthest sea,
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
even there Your hand will guide me; Your right hand will hold me fast.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
If I say, “Surely the darkness will hide me, and the light become night around me”—
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
even the darkness is not dark to You, but the night shines like the day, for darkness is as light to You.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
For You formed my inmost being; You knit me together in my mother’s womb.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
I praise You, for I am fearfully and wonderfully made. Marvelous are Your works, and I know this very well.
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
My frame was not hidden from You when I was made in secret, when I was woven together in the depths of the earth.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Your eyes saw my unformed body; all my days were written in Your book and ordained for me before one of them came to be.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
How precious to me are Your thoughts, O God, how vast is their sum!
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
If I were to count them, they would outnumber the grains of sand; and when I awake, I am still with You.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
O God, that You would slay the wicked— away from me, you bloodthirsty men—
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
who speak of You deceitfully; Your enemies take Your name in vain.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Do I not hate those who hate You, O LORD, and detest those who rise against You?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
I hate them with perfect hatred; I count them as my enemies.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Search me, O God, and know my heart; test me and know my concerns.
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
See if there is any offensive way in me; lead me in the way everlasting.

< Zabura 139 >