< Zabura 139 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
O Jehovah, thou have searched me, and known.
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
Thou know my sitting down and my rising up. Thou understand my thought afar off.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
Thou search out my path and my lying down, and are acquainted with all my ways.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
For there is not a word in my tongue, but, lo, O Jehovah, thou know it altogether.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
Thou have beset me behind and before, and laid thy hand upon me.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
Such knowledge is too wonderful for me. It is high, I cannot attain to it.
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Where shall I go from thy Spirit? Or where shall I flee from thy presence?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
If I ascend up into heaven, thou are there. If I make my bed in Sheol, behold, thou are there. (Sheol h7585)
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
If I take the wings of the morning, and dwell in the outermost parts of the sea,
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
even there thy hand shall lead me, and thy right hand shall hold me.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
If I say, Surely the darkness shall overwhelm me, and the light around me shall be night,
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
even the darkness hides not from thee, but the night shines as the day. The darkness and the light are both alike to thee.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
For thou formed my inward parts. Thou covered me in my mother's womb.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
I will give thanks to thee, for I am fearfully and wonderfully made. Wonderful are thy works, and that my soul knows right well.
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
My frame was not hidden from thee, when I was made in secret, curiously wrought in the lowest parts of the earth.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Thine eyes saw my unformed substance, and in thy book they were all written, even the days that were ordained, when as yet there was none of them.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
How precious also are thy thoughts to me, O God! How great is the sum of them!
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
I count them; they are more in number than the sand. When I awake, I am still with thee.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
Surely thou will kill the wicked, O God. Depart from me therefore, ye bloodthirsty men.
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
For they speak against thee wickedly, and thine enemies take it in vain.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Do I not hate them, O Jehovah, who hate thee? And am I not grieved with those who rise up against thee?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
I hate them with perfect hatred. They have become my enemies.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Search me, O God, and know my heart. Try me, and know my thoughts,
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
and see if there is any wicked way in me. And lead me in the way everlasting.

< Zabura 139 >