< Zabura 139 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
Een psalm van David, voor den opperzangmeester. HEERE! Gij doorgrondt en kent mij.
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
Gij weet mijn zitten en mijn opstaan; Gij verstaat van verre mijn gedachten.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
Gij omringt mijn gaan en mijn liggen; en Gij zijt al mijn wegen gewend.
4 Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
Als er nog geen woord op mijn tong is, zie, HEERE! Gij weet het alles.
5 Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
Gij bezet mij van achteren en van voren, en Gij zet Uw hand op mij.
6 Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
De kennis is mij te wonderbaar, zij is hoog, ik kan er niet bij.
7 Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
Waar zou ik heengaan voor Uw Geest en waar zou ik heenvlieden voor Uw aangezicht?
8 In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
Zo ik opvoer ten hemel, Gij zijt daar; of bedde ik mij in de hel, zie, Gij zijt daar. (Sheol h7585)
9 In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
Nam ik vleugelen des dageraads, woonde ik aan het uiterste der zee;
10 can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
Ook daar zou Uw hand mij geleiden, en Uw rechterhand zou mij houden.
11 In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
Indien ik zeide: De duisternis zal mij immers bedekken; dan is de nacht een licht om mij.
12 duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
Ook verduistert de duisternis voor U niet; maar de nacht licht als de dag; de duisternis is als het licht.
13 Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
Want Gij bezit mijn nieren; Gij hebt mij in mijner moeders buik bedekt.
14 Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
Ik loof U, omdat ik op een heel vreselijke wijze wonderbaarlijk gemaakt ben; wonderlijk zijn Uw werken! ook weet het mijn ziel zeer wel.
15 Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
Mijn gebeente was voor U niet verholen, als ik in het verborgene gemaakt ben, en als een borduursel gewrocht ben, in de nederste delen der aarde.
16 Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
Uw ogen hebben mijn ongevormden klomp gezien; en al deze dingen waren in Uw boek geschreven, de dagen als zij geformeerd zouden worden, toen nog geen van die was.
17 Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
Daarom, hoe kostelijk zijn mij, o God, Uw gedachten! hoe machtig veel zijn haar sommen!
18 A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
Zoude ik ze tellen? Harer is meer, dan des zands; word ik wakker, zo ben ik nog bij U.
19 Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
O God! dat Gij den goddeloze ombracht! en gij, mannen des bloeds, wijkt van mij!
20 Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
Die van U schandelijk spreken, en Uw vijanden ijdellijk verheffen.
21 Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
Zou ik niet haten HEERE! die U haten? en verdriet hebben in degenen, die tegen U opstaan?
22 Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
Ik haat hen met volkomen haat, tot vijanden zijn zij mij.
23 Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
Doorgrond mij, o God! en ken mijn hart; beproef mij, en ken mijn gedachten.
24 Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
En zie, of bij mij een schadelijke weg zij; en leid mij op den eeuwigen weg.

< Zabura 139 >