< Zabura 138 >
1 Ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; a gaban “alloli” zan rera yabo.
Давидів.
2 Zan rusuna ta wajen haikalinka mai tsarki zan kuma yabi sunanka saboda ƙaunarka da amincinka, saboda ka ɗaukaka a bisa kome sunanka da kuma maganarka.
Вклоняюсь до храму святого Твого, і сла́влю Іме́ння Твоє за Твоє милосердя й за правду Твою, бо звели́чив Ти був над усе Своє Йме́ння та слово Своє!
3 Sa’ad da na kira, ka amsa mini; ka sa na zama mai ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa ni.
Удень, як взива́ю, почуєш мене, підбадьо́рюєш силою душу мою!
4 Bari dukan sarakunan duniya su yabe ka, ya Ubangiji, sa’ad da suka ji maganganun bakinka.
Усі зе́мні царі прославля́ть Тебе, Господи, бу́дуть, бо почують вони слово уст Твоїх,
5 Bari su rera game da hanyoyin Ubangiji, gama ɗaukakar Ubangiji da girma take.
і бу́дуть співати про Господні доро́ги, бо слава Господня велика,
6 Ko da yake Ubangiji yana bisa, yakan dubi kāsassu, amma tun da nesa ya san masu girman kai.
бо високий Госпо́дь, — але бачить низько́го, а гордого Він пізнає́ іздале́ка!
7 Ko da na yi tafiya a tsakiyar wahala, kana kiyaye raina; ka miƙa hannunka a kan fushin maƙiyana, da hannunka na dama ka cece ni.
Якщо серед тісно́ти піду́, — Ти ожи́виш мене, на лютість моїх ворогів пошлеш руку Свою, і прави́ця Твоя допоможе мені, —
8 Ubangiji zai cika manufarsa a kaina; ƙaunarka, ya Ubangiji, madawwamiya ce har abada, kada ka ƙyale ayyukan hannuwanka.
для мене Господь оце виконає! Твоя милість, о Господи, вічна, — чи́нів Своєї руки не полиш!