< Zabura 138 >
1 Ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; a gaban “alloli” zan rera yabo.
“By David.” I will praise thee with my whole heart: before [thee], O God, will I sing praise unto thee.
2 Zan rusuna ta wajen haikalinka mai tsarki zan kuma yabi sunanka saboda ƙaunarka da amincinka, saboda ka ɗaukaka a bisa kome sunanka da kuma maganarka.
I will bow myself down before thy holy temple, and I will thank thy name for thy kindness and for thy truth; for thou hast magnified above all thy name thy promise.
3 Sa’ad da na kira, ka amsa mini; ka sa na zama mai ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa ni.
On the day when I called didst thou answer me, and raise me up with strength in my soul.
4 Bari dukan sarakunan duniya su yabe ka, ya Ubangiji, sa’ad da suka ji maganganun bakinka.
All the kings of the earth will give thanks unto thee, O Lord, when they hear the promises of thy mouth.
5 Bari su rera game da hanyoyin Ubangiji, gama ɗaukakar Ubangiji da girma take.
And they will sing on the ways of the Lord; for great is the glory of the Lord.
6 Ko da yake Ubangiji yana bisa, yakan dubi kāsassu, amma tun da nesa ya san masu girman kai.
For exalted is the Lord, yet doth he regard the lowly; but the proud he punisheth from afar.
7 Ko da na yi tafiya a tsakiyar wahala, kana kiyaye raina; ka miƙa hannunka a kan fushin maƙiyana, da hannunka na dama ka cece ni.
If I should walk in the midst of distress, thou wilt revive me: against the wrath of my enemies wilt thou stretch forth thy hand, and thy right hand will save me.
8 Ubangiji zai cika manufarsa a kaina; ƙaunarka, ya Ubangiji, madawwamiya ce har abada, kada ka ƙyale ayyukan hannuwanka.
The Lord will accomplish [all] in my behalf; O Lord, thy kindness endureth for ever: the works of thy own hands do not abandon.