< Zabura 138 >
1 Ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; a gaban “alloli” zan rera yabo.
A Psalme of David. I will praise thee with my whole heart: euen before the gods will I praise thee.
2 Zan rusuna ta wajen haikalinka mai tsarki zan kuma yabi sunanka saboda ƙaunarka da amincinka, saboda ka ɗaukaka a bisa kome sunanka da kuma maganarka.
I will worship toward thine holy Temple and praise thy Name, because of thy louing kindenesse and for thy trueth: for thou hast magnified thy Name aboue all things by thy word.
3 Sa’ad da na kira, ka amsa mini; ka sa na zama mai ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa ni.
When I called, then thou heardest me, and hast encreased strength in my soule.
4 Bari dukan sarakunan duniya su yabe ka, ya Ubangiji, sa’ad da suka ji maganganun bakinka.
All the Kings of the earth shall praise thee, O Lord: for they haue heard the wordes of thy mouth.
5 Bari su rera game da hanyoyin Ubangiji, gama ɗaukakar Ubangiji da girma take.
And they shall sing of the wayes of the Lord, because the glory of the Lord is great.
6 Ko da yake Ubangiji yana bisa, yakan dubi kāsassu, amma tun da nesa ya san masu girman kai.
For the Lord is high: yet he beholdeth the lowly, but the proude he knoweth afarre off.
7 Ko da na yi tafiya a tsakiyar wahala, kana kiyaye raina; ka miƙa hannunka a kan fushin maƙiyana, da hannunka na dama ka cece ni.
Though I walke in the middes of trouble, yet wilt thou reuiue me: thou wilt stretch foorth thine hand vpon the wrath of mine enemies, and thy right hand shall saue me.
8 Ubangiji zai cika manufarsa a kaina; ƙaunarka, ya Ubangiji, madawwamiya ce har abada, kada ka ƙyale ayyukan hannuwanka.
The Lord will performe his worke toward me: O Lord, thy mercie endureth for euer: forsake not the workes of thine handes.