< Zabura 138 >
1 Ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; a gaban “alloli” zan rera yabo.
A Psalm for David, of Aggaeus and Zacharias. I will give you thanks, O Lord, with my whole heart; and I will sing psalms to you before the angels; for you have heard all the words of my mouth.
2 Zan rusuna ta wajen haikalinka mai tsarki zan kuma yabi sunanka saboda ƙaunarka da amincinka, saboda ka ɗaukaka a bisa kome sunanka da kuma maganarka.
I will worship towards your holy temple, and give thanks to your name, on account of your mercy and your truth; for you have magnified your holy name above every thing.
3 Sa’ad da na kira, ka amsa mini; ka sa na zama mai ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa ni.
In whatever day I shall call upon you, hear me speedily; you shall abundantly provide me with your power in my soul.
4 Bari dukan sarakunan duniya su yabe ka, ya Ubangiji, sa’ad da suka ji maganganun bakinka.
Let all the kings of the earth, o Lord, give thanks to you; for they have heard all the words of your mouth.
5 Bari su rera game da hanyoyin Ubangiji, gama ɗaukakar Ubangiji da girma take.
And let them sing in the ways of the Lord; for great is the glory of the Lord.
6 Ko da yake Ubangiji yana bisa, yakan dubi kāsassu, amma tun da nesa ya san masu girman kai.
For the Lord is high, and [yet] regards the lowly; and he knows high things from afar off.
7 Ko da na yi tafiya a tsakiyar wahala, kana kiyaye raina; ka miƙa hannunka a kan fushin maƙiyana, da hannunka na dama ka cece ni.
Though I should walk in the midst of affliction, you will quicken me; you have stretched forth your hands against the wrath of mine enemies, and your right hand has saved me.
8 Ubangiji zai cika manufarsa a kaina; ƙaunarka, ya Ubangiji, madawwamiya ce har abada, kada ka ƙyale ayyukan hannuwanka.
O Lord, you shall recompense [them] on my behalf: your mercy, O Lord, [endures] for ever: overlook not the works of your hands.