< Zabura 135 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Deja que el Señor sea alabado. Oh siervos del Señor, alaben el nombre del Señor.
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
Tú que estás en la casa del Señor, y en los espacios abiertos de la casa de nuestro Dios,
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Alaben a Jah, porque él es bueno; hagan melodía a su nombre, porque es agradable.
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
Porque el Señor tomó consigo a Jacob, y a Israel por su propiedad.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
Sé que el Señor es grande, y que nuestro Señor es más grande que todos los demás dioses.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
El Señor hizo todo lo que le agradaba, en el cielo, en la tierra, en los mares y en todas las aguas profundas.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
Él hace que las nieblas suban desde los confines de la tierra; él hace llamas de trueno por la lluvia; Él envía los vientos desde sus almacenes.
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
El mató las primicias de Egipto, de hombres y de bestias.
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
Envió señales y maravillas en medio de ti, oh Egipto, sobre Faraón y sobre todos sus siervos.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
Él venció a las grandes naciones, y mató a los reyes fuertes;
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
Sehón, rey de los amorreos, y Og, rey de Basán, y todos los reinos de Canaán;
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
Y dieron su tierra por heredad, por heredad a Israel su pueblo.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
Oh Señor, tu nombre es eterno; y el recuerdo de ti no tendrá fin.
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
Porque el Señor juzgará la causa de su pueblo; tiene compasión de sus sirvientes.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
Las imágenes de las naciones son plata y oro, obra de manos de hombres.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Tienen bocas, pero ninguna voz; tienen ojos, pero no ven;
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
Tienen oídos, pero no oyen; y no hay aliento en sus bocas.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Los que los hacen son como ellos; y también lo es todo el que pone su esperanza en ellos.
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
Alaben a Jehová, oh hijos de Israel; alaben á Jehová, oh hijos de Aarón.
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
Alaben al Señor, hijos de Leví, alaben todos los adoradores del Señor.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Bendito sea el Señor desde Sión, el Señor cuya casa está en Jerusalén, sea alabado Jehová.