< Zabura 135 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Alabád el nombre de Jehová, alabád siervos de Jehová.
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
Los que estáis en la casa de Jehová, en los patios de la casa de nuestros Dios.
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Alabád a Jehová, porque es bueno Jehová: cantád salmos a su nombre, porque es suave.
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
Porque Jehová ha escogido a Jacob para sí, a Israel por su posesión.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
Porque yo sé que Jehová es grande, y el Señor nuestro mayor que todos los dioses.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
Todo lo que quiso Jehová, hizo en los cielos y en la tierra, en las mares, y en todos los abismos.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
El que hace subir las nubes del cabo de la tierra: hizo los relámpagos para la lluvia; el que saca los vientos de sus tesoros.
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
El que hirió a los primogénitos de Egipto desde el hombre hasta la bestia.
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
Envió señales y prodigios en medio de ti, o! Egipto: en Faraón, y en todos sus siervos.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
El que hirió a muchas naciones; y mató a reyes poderosos:
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
A Sejón rey Amorreo, y a Og rey de Basán, y a todos los reinos de Canaán.
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
Y dio la tierra de ellos en heredad: en heredad a Israel su pueblo.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
Jehová, tu nombre es eterno: Jehová, tu memoria para generación y generación.
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
Porque Jehová juzgará a su pueblo; y sobre sus siervos se arrepentirá.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
Los ídolos de los Gentiles son plata y oro: obra de manos de hombre.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Tienen boca, y no hablan: tienen ojos y no ven.
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
Tienen orejas y no escuchan; tampoco hay espíritu en sus bocas.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Como ellos sean los que los hacen; y todos los que en ellos confían.
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
Casa de Israel bendecíd a Jehová: Casa de Aarón bendecíd a Jehová:
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
Casa de Leví bendecíd a Jehová: los que teméis a Jehová, bendecíd a Jehová.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Bendito Jehová de Sión, el que mora en Jerusalem. Alelu- Jah.

< Zabura 135 >