< Zabura 135 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Louvae ao Senhor. Louvae o nome do Senhor; louvae-o, servos do Senhor.
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
Vós que assistis na casa do Senhor, nos atrios da casa do nosso Deus.
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Louvae ao Senhor, porque o Senhor é bom: cantae louvores ao seu nome, porque é agradavel.
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
Porque o Senhor escolheu para si a Jacob, e a Israel para seu proprio thesouro.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
Porque eu conheço que o Senhor é grande e que o nosso Deus está acima de todos os deuses.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
Tudo o que o Senhor quiz fez, nos céus e na terra, nos mares e em todos os abysmos.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
Faz subir os vapores das extremidades da terra; faz os relampagos para a chuva; produz os ventos dos seus thesouros.
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
O que feriu os primogenitos do Egypto, desde os homens até ás bestas.
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
O que enviou signaes e prodigios no meio de ti, ó Egypto, contra Pharaó e contra os seus servos.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
O que feriu muitas nações, e matou poderosos reis;
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
A Sehon, rei dos amorrheos, e a Og, rei de Basan, e a todos os reinos de Canaan.
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
E deu a sua terra em herança, em herança a Israel, seu povo.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
O teu nome, ó Senhor, dura perpetuamente; e a tua memoria, ó Senhor, de geração em geração.
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
Pois o Senhor julgará o seu povo, e se arrependerá com respeito aos seus servos.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
Os idolos das nações são prata e oiro, obra das mãos dos homens.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Teem bocca, mas não fallam; teem olhos, e não vêem.
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
Teem ouvidos, mas não ouvem, nem ha respiro algum nas suas boccas.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Similhantes a elles se tornem os que os fazem, e todos os que confiam n'elles.
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
Casa d'Israel, bemdizei ao Senhor; casa d'Aarão bemdizei ao Senhor.
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
Casa de Levi, bemdizei ao Senhor: vós, os que temeis ao Senhor, louvae ao Senhor.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Bemdito seja o Senhor desde Sião, que habita em Jerusalem. Louvae ao Senhor.

< Zabura 135 >