< Zabura 135 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Halleluja! Lov Herrens navn, lov, I Herrens tjenere,
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
I som står i Herrens hus, i forgårdene til vår Guds hus!
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Lov Herren! for Herren er god, lovsyng hans navn! for det er liflig.
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
For Herren har utvalgt sig Jakob, Israel til sin eiendom.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
Jeg vet at Herren er stor, og vår Herre større enn alle guder.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
Herren gjør alt det han vil, i himmelen og på jorden, i havene og alle dyp,
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
han som lar regnskyer stige op fra jordens ende, gjør lyn til regn, fører vind ut av sine forrådshus,
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
han som slo de førstefødte i Egypten, både mennesker og fe.
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
som sendte tegn og under midt i dig, Egypten, mot Farao og mot alle hans tjenere,
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
han som slo mange hedningefolk og drepte mektige konger,
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
Sihon, amorittenes konge, og Og, Basans konge, og alle Kana'ans kongeriker,
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
og gav deres land til arv, gav Israel, sitt folk, det til arv.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
Herre, ditt navn blir til evig tid, Herre, ditt minne fra slekt til slekt.
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
For Herren skal dømme sitt folk, og han skal miskunne sig over sine tjenere.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
Hedningenes avguder er sølv og gull, et verk av menneskers hender.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
De har munn, men taler ikke; de har øine, men ser ikke;
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
de har ører, men hører ikke, og det er ikke nogen ånde i deres munn.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Som de selv er, blir de som gjør dem, hver den som setter sin lit til dem.
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
Israels hus, lov Herren! Arons hus, lov Herren!
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
Levis hus, lov Herren! I som frykter Herren, lov Herren!
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Lovet være Herren fra Sion, han som bor i Jerusalem! Halleluja!

< Zabura 135 >