< Zabura 135 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Alleluia. Laudate nomen Domini, laudate servi Dominum:
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
Qui statis in domo Domini, in atriis domus Dei nostri.
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Laudate Dominum, quia bonus Dominus: psallite nomini eius, quoniam suave.
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
Quoniam Iacob elegit sibi Dominus Israel in possessionem sibi.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
Quia ego cognovi quod magnus est Dominus, et Deus noster prae omnibus diis.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
Omnia quaecumque voluit, Dominus fecit in caelo, in terra, in mari, et in omnibus abyssis.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
Educens nubes ab extremo terrae: fulgura in pluviam fecit. Qui producit ventos de thesauris suis:
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
qui percussit primogenita Aegypti ab homine usque ad pecus.
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
Et misit signa, et prodigia in medio tui Aegypte: in Pharaonem, et in omnes servos eius.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
Qui percussit gentes multas: et occidit reges fortes:
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
Sehon regem Amorrhaeorum, et Og regem Basan, et omnia regna Chanaan.
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
Et dedit terram eorum hereditatem, hereditatem Israel populo suo.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
Domine nomen tuum in aeternum: Domine memoriale tuum in generatione et generationem.
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
Quia iudicabit Dominus populum suum: et in servis suis deprecabitur.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
Simulacra Gentium argentum, et aurum, opera manuum hominum.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Os habent, et non loquentur: oculos habent, et non videbunt.
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
Aures habent, et non audient: neque enim est spiritus in ore ipsorum.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Similes illis fiant qui faciunt ea: et omnes, qui confidunt in eis.
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
Domus Israel benedicite Domino: domus Aaron benedicite Domino.
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
Domus Levi benedicite Domino: qui timetis Dominum, benedicite Domino.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Benedictus Dominus ex Sion, qui habitat in Ierusalem.

< Zabura 135 >