< Zabura 135 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Halleluja! Preiset den Namen des HERRN, preist ihn, ihr Diener des HERRN,
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
die ihr stehet im Hause des HERRN, in den Höfen am Haus unsers Gottes!
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Preiset den HERRN, denn gütig ist der HERR; lobsingt seinem Namen, denn lieblich ist er!
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
Denn Jakob hat der HERR sich erwählt und Israel sich zum Eigentum erkoren.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
Ja, ich weiß es: groß ist der HERR, und unser Gott steht über allen Göttern;
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
alles, was dem HERRN gefällt, das führt er aus im Himmel und auf Erden, in den Meeren und allen Tiefen.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
Er ist’s, der Wolken heraufführt vom Ende der Erde, der Blitze bei Gewitterregen schafft, der den Wind aus seinen Speichern herausläßt.
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
Er war’s, der Ägyptens Erstgeburten schlug unter Menschen wie beim Vieh;
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
der Zeichen und Wunder sandte in deine Mitte, Ägypten, gegen den Pharao und all seine Knechte.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
Er war’s, der viele Völker schlug und mächtige Könige tötete:
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
Sihon, den König der Amoriter, und Og, den König von Basan, und alle Königreiche Kanaans,
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
und ihr Land als Erbbesitz hingab, als Erbe seinem Volke Israel.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
O HERR, dein Name währt ewig, dein Gedächtnis, o HERR, von Geschlecht zu Geschlecht
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
denn der HERR schafft Recht seinem Volk und erbarmt sich über seine Knechte.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
Die Götzen der Heiden sind Silber und Gold, das Machwerk von Menschenhänden;
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
sie haben einen Mund und können nicht reden, haben Augen und sehen nicht;
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
sie haben Ohren und können nicht hören, auch ist kein Odem in ihrem Munde.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Ihnen gleich sind ihre Verfertiger, jeder, der auf sie vertraut.
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
Ihr vom Hause Israel, preiset den HERRN! Ihr vom Hause Aaron, preiset den HERRN!
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
Ihr vom Hause Levi, preiset den HERRN! Ihr, die ihr fürchtet den HERRN, preiset den HERRN!
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Gepriesen sei der HERR von Zion aus, er, der da wohnt in Jerusalem! Halleluja!

< Zabura 135 >