< Zabura 135 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Alléluia.
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
Qui demeurez dans la maison du Seigneur, dans les parvis de la maison de notre Dieu.
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Louez le Seigneur, parce que le Seigneur est bon: chantez son nom, parce que son nom est doux,
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
Parce que le Seigneur s’est choisi Jacob et Israël pour sa possession.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
Car moi j’ai connu que le Seigneur est grand, et que notre Dieu est au-dessus de tous les dieux.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
Tout ce qu’il a voulu, le Seigneur l’a fait dans le ciel, sur la terre, dans la mer et dans tous les abîmes.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
Amenant des nuages de l’ extrémité de la terre, il a changé des éclairs en pluie.
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
C’est lui qui a frappé les premiers-nés d’Égypte, depuis l’homme jusqu’à la bête.
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
Et il a envoyé des signes et des prodiges au milieu de toi, ô Égypte, contre Pharaon et contre tous ses serviteurs.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
C’est lui qui a frappé des nations nombreuses, et a tué des rois puissants,
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
Séhon, roi des Amorrhéens, et Og, roi de Basan, et tous les royaumes de Chanaan.
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
Et il a donné leur terre en héritage, en héritage à Israël son peuple.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
Seigneur, votre nom subsistera éternellement, et votre souvenir dans toutes les générations.
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
Parce que le Seigneur jugera son peuple, et il sera imploré par ses serviteurs.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
Les simulacres des nations sont de l’argent et de l’or; des ouvrages de main d’hommes.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Ils ont une bouche, et ils ne parleront pas; ils ont des yeux, et ne verront pas.
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
Ils ont des oreilles, et ils n’entendront pas, car il n’y a pas de souffle dans leur bouche.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Qu’ils leur deviennent semblables, ceux qui les font, et tous ceux qui se confient en elles.
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
Maison d’Israël, bénissez le Seigneur; maison d’Aaron, bénissez le Seigneur.
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
Maison de Lévi, bénissez le Seigneur; vous qui craignez le Seigneur, bénissez le Seigneur.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Béni soit le Seigneur du haut de Sion, lui qui habite dans Jérusalem.