< Zabura 135 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Alléluia! Louez le nom de l’Eternel louez-le, serviteurs de l’Eternel,
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
qui vous tenez dans la maison du Seigneur, dans les parvis de la maison de notre Dieu.
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Louez le Seigneur, car l’Eternel est bon, célébrez son nom, car il est doux,
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
car le Seigneur a fait choix de Jacob; d’Israël il a fait son peuple d’élection.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
Oui, je sais que grand est l’Eternel, grand notre maître plus que toutes les divinités.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
Tout ce que veut l’Eternel, il le fait, dans les cieux et sur la terre, sur les mers et dans toutes les profondeurs de l’abîme.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
Il amène les nuages des extrémités de la terre; il accompagne d’éclairs la pluie, fait s’échapper le vent de ses réservoirs.
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
C’Est lui qui a frappé les premiers-nés d’Egypte, parmi les hommes et parmi les animaux;
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
il a envoyé signes et prodiges sur ton sol, ô Egypte, contre Pharaon et tous ses serviteurs.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
Il a abattu des peuples puissants, fait périr des rois formidables,
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
Sihon, roi des Amorréens, Og, roi de Basan, et tous les souverains de Canaan,
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
pour donner leur pays en héritage, en héritage à Israël, son peuple.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
Eternel, ton nom dure à jamais, Eternel, ta gloire d’âge en âge.
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
Car l’Eternel fait justice à son peuple et il est plein de commisération pour ses serviteurs.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
Les idoles des nations, faites d’argent et d’or, sont l’œuvre de mains humaines.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Elles ont une bouche et ne parlent point, des yeux et ne voient pas;
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
elles ont des oreilles et n’entendent point, il n’y a même pas un souffle dans leur bouche.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Puissent devenir comme elles ceux qui les fabriquent, quiconque met en elles sa confiance!
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
Maison d’Israël, bénissez le Seigneur! Maison d’Aaron, bénissez le Seigneur!
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
Maison de Lévi, bénissez le Seigneur! Adorateurs de l’Eternel, bénissez le Seigneur!
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Que l’Eternel soit béni de Sion, Lui qui demeure à Jérusalem. Alléluia!

< Zabura 135 >