< Zabura 135 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Alleluya. Herie ye the name of the Lord; ye seruauntis of the Lord, herie ye.
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
Ye that stonden in the hous of the Lord; in the hallis of `the hous of oure God.
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Herie ye the Lord, for the Lord is good; singe ye to his name, for it is swete.
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
For the Lord chees Jacob to him silf; Israel in to possessioun to him silf.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
For Y haue knowe, that the Lord is greet; and oure God bifore alle goddis.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
The Lord made alle thingis, what euere thingis he wolde, in heuene and in erthe; in the see, and in alle depthis of watris.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
He ledde out cloudis fro the ferthest part of erthe; and made leitis in to reyn. Which bringith forth wyndis fro hise tresours;
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
which killide the firste gendrid thingis of Egipt, fro man `til to beeste.
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
He sente out signes and grete wondris, in the myddil of thee, thou Egipt; in to Farao and in to alle hise seruauntis.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
Which smoot many folkis; and killide stronge kingis.
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
Seon, the king of Ammorreis, and Og, the king of Basan; and alle the rewmes of Chanaan.
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
And he yaf the lond of hem eritage; eritage to Israel, his puple.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
Lord, thi name is with outen ende; Lord, thi memorial be in generacioun and in to generacioun.
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
For the Lord schal deme his puple; and he schal be preied in hise seruauntis.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
The symulacris of hethene men ben siluer and gold; the werkis of the hondis of men.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Tho han a mouth, and schulen not speke; tho han iyen, and schulen not se.
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
Tho han eeris, and schulen not here; for `nether spirit is in the mouth of tho.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Thei that maken tho, be maad lijk tho; and alle that tristen in tho.
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
The hous of Israel, blesse ye the Lord; the hous of Aaron, blesse ye the Lord.
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
The hous of Leuy, blesse ye the Lord; ye that dreden the Lord, `blesse ye the Lord.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Blessid be the Lord of Syon; that dwellith in Jerusalem.