< Zabura 135 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Praise Yahweh! You who (do work for/serve) Yahweh, praise him!
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
You who stand in the temple of Yahweh our God and in the surrounding courtyard, praise him [MTY]!
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Praise Yahweh, because he does good things [for us]; sing to him [MTY], because he is kind [to us].
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
He has chosen [us, the descendants of] Jacob; he has chosen [us] Israelis to belong to him [DOU].
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
I know that Yahweh is great; he is greater than all the gods.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
Yahweh does whatever he desires to do, in heaven and on the earth and in the seas/oceans, [down] to the bottom of the seas.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
He is the one who causes clouds to appear from very distant places on the earth; he sends lightning with the rain, and he brings the winds from the places where he stores them.
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
He is the one who killed [all] the firstborn [males] in Egypt, the firstborn of people and of animals.
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
There he performed many kinds of miracles [DOU] to punish the king and all his officials.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
He destroyed many nations and the powerful kings [who ruled them]:
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
Sihon, the king of the Amor people-group, and Og, the king of Bashan [region], and all the other kings in Canaan [land].
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
Then he gave their land to [us] Israeli people to belong to us [forever].
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
Yahweh your name will endure forever, and people who are not yet born will remember the great things [that you have done].
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
Yahweh, [you] declare that we your people (are innocent/have not done things that are wrong), and you are merciful to us.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
But the idols that the [other] people-groups [worship] are only [statues made of] silver and gold, things that humans have made.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Their idols have mouths, but they cannot say [anything]; they have eyes, but they cannot see [anything].
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
They have ears, but they cannot hear [anything], and they are not [even able to] breathe.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
The people who make those idols are as [powerless as] those idols, and those who trust in those idols [can accomplish no more than] their idols can!
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
[My fellow] Israelis, praise Yahweh! You [priests] who are descended from Aaron, praise Yahweh!
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
You [men] who are descended from Levi, [you who assist the priests], praise Yahweh! [All] you who revere Yahweh, praise him!
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Praise Yahweh in [the temple on] Zion [Hill] in Jerusalem, where he lives! Praise Yahweh!

< Zabura 135 >