< Zabura 135 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
Praise ye the name of the Lord: O you his servants, praise the Lord:
2 ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
You that stand in the house of the Lord, in the courts of the house of our God.
3 Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
Praise ye the Lord, for the Lord is good: sing ye to his name, for it is sweet.
4 Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
For the Lord hath chosen Jacob unto himself: Israel for his own possession.
5 Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
For I have known that the Lord is great, and our God is above all gods.
6 Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
Whatsoever the Lord hath pleased he hath done, in heaven, in earth, in the sea, and in all the deeps.
7 Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
He bringeth up clouds from the end of the earth: he hath made lightnings for the rain. He bringeth forth winds out of his stores:
8 Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
He slew the firstborn of Egypt from man even unto beast.
9 Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
He sent forth signs and wonders in the midst of thee, O Egypt: upon Pharao, and upon all his servants.
10 Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
He smote many nations, and slew mighty kings:
11 Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
Sehon king of the Amorrhites, and Og king of Basan, and all the kingdoms of Chanaan.
12 ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
And gave their land for an inheritance, for an inheritance to his people Israel.
13 Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
Thy name, O Lord, is for ever: thy memorial, O Lord, unto all generations.
14 Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
For the Lord will judge his people, and will be entreated in favour of his servants.
15 Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
The idols of the Gentiles are silver and gold, the works of men’s hands.
16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
They have a mouth, but they speak not: they have eyes, but they see not.
17 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
They have ears, but they hear not: neither is there any breath in their mouths.
18 Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
Let them that make them be like to them: and every one that trusteth in them.
19 Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
Bless the Lord, O house of Israel: bless the Lord, O house of Aaron.
20 Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
Bless the Lord, O house of Levi: you that fear the Lord, bless the Lord.
21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.
Blessed be the Lord out of Sion, who dwelleth in Jerusalem.