< Zabura 131 >

1 Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Zuciyata ba mai girman kai ba ce, ya Ubangiji, idanuna ba sa fariya; ban dami kaina da manyan al’amura ba ko abubuwan da suka sha ƙarfina.
Cantique de Mahaloth, de David. Ô Éternel! mon cœur ne s'est point élevé, et mes yeux ne se sont point haussés, et je n'ai point marché en des choses grandes et merveilleuses au-dessus de ma portée.
2 Amma na haƙura na kuma kwantar da raina; kamar yaron da aka yaye tare da mahaifiyarsa, kamar yaron da aka yaye haka raina yake a cikina.
N'ai-je point soumis et fait taire mon cœur, comme celui qui est sevré fait envers sa mère; mon cœur est en moi, comme celui qui est sevré.
3 Ya Isra’ila, sa zuciyarka ga Ubangiji yanzu da har abada kuma.
Israël attends-toi à l'Eternel dès maintenant et à toujours.

< Zabura 131 >