< Zabura 130 >
1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Пісня сходження. Із глибин кличу я до Тебе, Господи.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Володарю, почуй же мій голос, нехай схиляться вуха Твої до голосу благання мого!
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Якщо беззаконня Ти, Господи, пильнуватимеш, хто ж встояти зможе, Владико?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Але в Тебе прощення, щоб мали страх [перед Тобою].
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
Я покладаю надію на Господа, надію має душа моя, і на слово Його сподіваюся.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
Душа моя на Владику чекає більше, ніж сторожа ранку, так, більше, ніж сторожа ранку!
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Нехай Ізраїль сподівається на Господа, адже в Господа милість і велике визволення – у Нього.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
І Він визволить Ізраїля від усіх його беззаконь.