< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Un cántico para los peregrinos que van a Jerusalén. Señor, clamo a ti desde lo más profundo de mi dolor.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Por favor escucha mi llanto, presta atención a lo que pido.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Señor, si guardaras una lista de nuestros pecados, ¿Quién podría escapar de ser condenado?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Pero tú eres un Dios perdonador y por eso debes ser respetado.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
Yo espero en el Señor, espero ansiosamente, porque confío en su palabra.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
Anhelo que el Señor vuelva, más que los vigilantes añorando el amanecer.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Israel, deposita tus esperanzas en el Señor, porque el Señor nos ama con su inmenso amor, y su salvación no conoce límites.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
Él redimirá a Israel de todos sus pecados.

< Zabura 130 >