< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Cántico gradual. Desde lo más profundo clamo a Ti, Yahvé,
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Señor, oye mi voz. Estén tus oídos atentos al grito de mi súplica.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Si Tú recordaras las iniquidades, oh Yah, Señor ¿quién quedaría en pie?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Mas en Ti esta el perdón de los pecados, a fin de que se te venere.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
Espero en Yahvé, mi alma confía en su palabra. Aguardando está
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
mi alma al Señor, más que los centinelas el alba. Más que los centinelas con la aurora
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
cuenta Israel con Yahvé, porque en Yahvé está la misericordia, y con Él copiosa redención.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
Y Él mismo redimirá a Israel de todas sus iniquidades.

< Zabura 130 >