< Zabura 130 >
1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Песнь восхождения. Из глубины взываю к Тебе, Господи.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Господи! услышь голос мой. Да будут уши Твои внимательны к голосу молений моих.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Если Ты, Господи, будешь замечать беззакония, - Господи! кто устоит?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Но у Тебя прощение, да благоговеют пред Тобою.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
Надеюсь на Господа, надеется душа моя; на слово Его уповаю.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
Душа моя ожидает Господа более, нежели стражи - утра, более, нежели стражи - утра.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Да уповает Израиль на Господа, ибо у Господа милость и многое у Него избавление,
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
и Он избавит Израиля от всех беззаконий его.