< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Uma Canção de Ascensões. Out das profundezas que eu chorei para você, Javé.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Senhor, ouve minha voz. Que seus ouvidos estejam atentos à voz das minhas petições.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Se você, Yah, mantivesse um registro de pecados, Senhor, quem poderia ficar de pé?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Mas há perdão com você, portanto, você é temido.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
Espero por Yahweh. Minha alma espera. Espero em sua palavra.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
Minha alma anseia pelo Senhor mais do que os guardas anseiam pela manhã, mais do que vigias para a manhã.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Israel, esperança em Yahweh, pois há bondade amorosa com Yahweh. A redenção abundante está com ele.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
Ele redimirá Israel de todos os seus pecados.

< Zabura 130 >