< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Cântico dos degraus: Das profundezas clamo a ti, SENHOR.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Ouve, Senhor, a minha voz; sejam teus ouvidos atentos à voz de minhas súplicas.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Se tu, SENHOR, considerares todas as perversidades, quem resistirá, Senhor?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Mas contigo está o perdão, para que tu sejas temido.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
Mantenho esperança no SENHOR, a minha alma espera; e persisto em sua palavra.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
Minha alma [espera ansiosamente] pelo Senhor, mais que os guardas [esperam] pela manhã, [mais] que os vigilantes pelo alvorecer.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Espere, Israel, pelo SENHOR; porque com o SENHOR há bondade, e com ele muito resgate.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
E ele resgatará Israel de todas as suas perversidades.

< Zabura 130 >