< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
canticum graduum de profundis clamavi ad te Domine
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Domine exaudi vocem meam fiant aures tuae intendentes in vocem deprecationis meae
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
si iniquitates observabis Domine Domine quis sustinebit
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
quia apud te propitiatio est propter legem tuam sustinui te Domine sustinuit anima mea in verbum eius
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
speravit anima mea in Domino
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
a custodia matutina usque ad noctem speret Israhel in Domino
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
quia apud Dominum misericordia et copiosa apud eum redemptio
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
et ipse redimet Israhel ex omnibus iniquitatibus eius

< Zabura 130 >