< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
京まうでの歌 ああヱホバよわれふかき淵より汝をよべり
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
主よねがはくはわが聲をきい汝のみみをわが懇求のこゑにかたぶけたまヘ
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
ヤハよ主よなんぢ若もろもろの不義ふぎに目をとめたまはば誰たれかよく立たつことをえんや
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
されどなんぢに赦あれば人におそれかしこまれ給ふべし
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
我ヱホバを俟望む わが霊魂はまちのぞむ われはその聖言によりて望をいだく
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
わがたましひは衛士があしたを待にまさり 誠にゑじが旦をまつにまさりて主をまてり
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
イスラエルよヱホバによりて望をいだけ そはヱホバにあはれみあり またゆたかなる救贖あり
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
ヱホバはイスラエルをそのもろもろの邪曲よりあがなひたまはん

< Zabura 130 >