< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
שִׁיר הַֽמַּעֲלוֹת מִמַּעֲמַקִּים קְרָאתִיךָ יְהֹוָֽה׃
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
אֲדֹנָי שִׁמְעָה בְקוֹלִי תִּהְיֶינָה אׇזְנֶיךָ קַשֻּׁבוֹת לְקוֹל תַּחֲנוּנָֽי׃
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
אִם־עֲוֺנוֹת תִּשְׁמׇר־יָהּ אֲדֹנָי מִי יַעֲמֹֽד׃
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
כִּֽי־עִמְּךָ הַסְּלִיחָה לְמַעַן תִּוָּרֵֽא׃
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
קִוִּיתִי יְהֹוָה קִוְּתָה נַפְשִׁי וְֽלִדְבָרוֹ הוֹחָֽלְתִּי׃
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
נַפְשִׁי לַאדֹנָי מִשֹּׁמְרִים לַבֹּקֶר שֹׁמְרִים לַבֹּֽקֶר׃
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
יַחֵל יִשְׂרָאֵל אֶל־יְהֹוָה כִּֽי־עִם־יְהֹוָה הַחֶסֶד וְהַרְבֵּה עִמּוֹ פְדֽוּת׃
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
וְהוּא יִפְדֶּה אֶת־יִשְׂרָאֵל מִכֹּל עֲוֺנֹתָֽיו׃

< Zabura 130 >