< Zabura 130 >
1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Ein Stufenlied. / Aus Tiefen hab ich, Jahwe, zu dir gerufen.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Adonái, hör meine Stimme! / Laß doch deine Ohren merken / Auf mein lautes Flehn!
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Wenn du Sünden anrechnest, Jah, / Adonái, wer kann dann bestehn?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Ja, du vergibst, / Damit man dich fürchte.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
Jahwes habe ich stets geharrt; / Es hat meine Seele geharrt, / Schon immer hoffte ich auf sein Wort.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
Meine Seele harrt Adonáis, / Mehr, als Wächter des Morgens harren, / Ja, Wächter des Morgens.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Israel, harr auf Jahwe! / Denn bei Jahwe ist die Gnade, / Und reichlich ist bei ihm Erlösung.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
Ja, er wird Israel erlösen / Von allen seinen Sünden.