< Zabura 130 >
1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Cantique de Maaloth. O Éternel, je t'invoque des lieux profonds.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Seigneur, écoute ma voix! Que tes oreilles soient attentives à la voix de mes supplications!
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Éternel, si tu prends garde aux iniquités, Seigneur, qui subsistera?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Mais le pardon se trouve auprès de toi, afin qu'on te craigne.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
J'ai attendu l'Éternel; mon âme l'a attendu, et j'ai eu mon espérance en sa parole.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
Mon âme attend le Seigneur, plus que les sentinelles n'attendent le matin.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Israël, attends-toi à l'Éternel, car la miséricorde est auprès de l'Éternel, et la rédemption se trouve en abondance auprès de lui.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
Et lui-même rachètera Israël de toutes ses iniquités.