< Zabura 130 >
1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
En Jérusalem. Des profondeurs de l'abîme, j'ai crié vers toi, Seigneur.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Seigneur, écoute ma voix; que ton oreille soit attentive à la voix de ma prière.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Si tu regardes nos iniquités, Seigneur, Seigneur, qui soutiendra ton regard?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Car la miséricorde est en toi; à cause de ton nom, je t'ai attendu, Seigneur. Mon âme a mis son attente en ta parole.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
Mon âme a espéré dans le Seigneur.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
Que depuis la veille du matin jusqu'à la nuit, Israël espère dans le Seigneur.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Car la miséricorde est dans le Seigneur, et une abondante rédemption est en lui.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
Et c'est lui qui rachètera Israël de toutes ses iniquités.