< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Cantique des degrés. Des profondeurs de l’abîme, je t’invoque, ô Eternel!
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Seigneur, écouté ma voix, que tes oreilles soient attentives aux accents de mes supplications.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Si tu tenais compte de nos fautes, Seigneur, qui pourrait subsister devant toi?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
Mais chez toi l’emporte le pardon, de telle sorte qu’on te révère.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
J’Espère en l’Eternel, mon âme est pleine d’espoir, et j’ai toute confiance en sa parole.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
Mon âme attend le Seigneur plus ardemment que les guetteurs le matin, oui, que les guetteurs n’attendent le matin.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Qu’Israël mette son attente en l’Eternel, car chez l’Eternel domine la grâce et abonde le salut.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
C’Est lui qui affranchit Israël de toutes ses fautes.

< Zabura 130 >