< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
A Song of Ascents. Out of the depths, have I cried unto thee, O Yahweh.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
O My Lord! hearken thou unto my voice, —Let thine ears be attentive to the voice of my supplications,
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
If, iniquities, thou shouldest mark, O Yah, O My Lord, who could stand?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
But, with thee, is forgiveness, that thou mayest be revered.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
I have waited for Yahweh, My soul hath waited for his word;
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
I have hoped, O my soul, for My Lord, more than they who watch for the morning, who watch for the morning.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Wait, O Israel, for Yahweh, —for, with Yahweh, is lovingkindness, and there aboundeth with him—redemption.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
He, therefore, will redeem Israel from all his iniquities.

< Zabura 130 >