< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
A Song of Ascents. Out of the depths have I cried unto thee, O LORD.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Lord, hear my voice: let thine ears be attentive to the voice of my supplications.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
If thou, LORD, shouldest mark iniquities, O Lord, who shall stand?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
But there is forgiveness with thee, that thou mayest be feared.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
I wait for the LORD, my soul doth wait, and in his word do I hope.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
My soul [looketh] for the Lord, more than watchmen [look] for the morning; [yea, more than] watchmen for the morning.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
O Israel, hope in the LORD; for with the LORD there is mercy, and with him is plenteous redemption.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
And he shall redeem Israel from all his iniquities.

< Zabura 130 >