< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
A song of degrees. Out of the deepe places haue I called vnto thee, O Lord.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Lord, heare my voyce: let thine eares attend to the voyce of my prayers.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
If thou, O Lord, straightly markest iniquities, O Lord, who shall stand?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
But mercie is with thee, that thou mayest be feared.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
I haue waited on the Lord: my soule hath waited, and I haue trusted in his worde.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
My soule waiteth on the Lord more then the morning watch watcheth for the morning.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Let Israel waite on the Lord: for with the Lord is mercie, and with him is great redemption.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
And he shall redeeme Israel from all his iniquities.

< Zabura 130 >