< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
A song for pilgrims going up to Jerusalem. Lord, I cry out to you from the depths of my pain.
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Please listen to my cry, and pay attention to what I'm asking.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
Lord, if you kept a list of sins, who could escape being condemned?
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
But you are forgiving so that we might respect you.
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
I'm waiting for the Lord, longingly waiting, for I trust in his word.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
I long for the Lord to come, more than watchmen longing for the dawn to come, more than watchmen longing for the dawn to come.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Israel, put your hope in the Lord, for the Lord loves us with a trustworthy love and his salvation knows no limits.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
He will save Israel from every sin.

< Zabura 130 >