< Zabura 130 >

1 Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
Out of the depths I have cried to thee, O Lord:
2 Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
Lord, hear my voice. Let thy ears be attentive to the voice of my supplication.
3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
If thou, O Lord, wilt mark iniquities: Lord, who shall stand it.
4 Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
For with thee there is merciful forgiveness: and by reason of thy law, I have waited for thee, O Lord. My soul hath relied on his word:
5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
My soul hath hoped in the Lord.
6 Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
From the morning watch even until night, let Israel hope in the Lord.
7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
Because with the Lord there is mercy: and with him plentiful redemption.
8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.
And he shall redeem Israel from all his iniquities.

< Zabura 130 >